Sojojin Sun Gano Wurin Ƙera Bindiga A Jihar Filato

Sojojin rundunar samar da tsaro a jihar Filato ta Operation Safe Haven sun bankaɗo wata haramtacciyar masana’antar ƙera makamai dake ƙauyen Pakachi a ƙaramar hukumar Mangu ta jihar Filato.

Jami’in ƴada labarai na rundunar, James Oya ya ce sojojin sun gano makamai da dama da kuma harsasai tare da kama mutum guda a farmakin da suka kai masana’antar.

Oya ya ce an samu nasarar gano masana’antar ne sakamakon cigaba da jajircewa da rundunar take na raba jihar da duk wasu ɓata gari dake tayar da zaune tsaye.

Ya ce an gano wurin ne a wani saman tsauni dake kauyen na Pakachi.

Ya ƙara da cewa wanda ake zargin shi ne mai masana’antar ya cika wandonsa da iska amma na cigaba kokarin ganin an kamo shi domin ya fuskanci hukunci.

Bindigogin da aka gano a wurin sun haɗa da AK-47 guda biyar da kuma ƙaramar bindiga ƙirar Pistol guda 11.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

Ɗan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...