Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan ta’adda 191 tare da kama 184

Rundunar sojojin Najeriya ta bayyana hakan ne a wata sanarwa wacce aka fitar bayan wani taron manema labarai da rundunar ta yi a Abuja a ranar Alhamis, inda ta bayyana wasu nasarori da sojojin suka samu cikin mako guda.

Rundunar tsaron Nijeriya ta ce dakarun tsaron kasar sun kashe ‘yan ta’adda 191, sun kama 184 sannan sun kubutar da mutum 91 da aka yi garkuwa da su a wasu ayyukan samame da suka ƙaddamar a faɗin ƙasar.

Rundunar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da TRT Afrika ta samu, wacce aka fitar bayan wani taron manema labarai da rundunar ta yi a Abuja a ranar Alhamis, inda ta bayyana wasu nasarori da sojojin suka samu cikin mako guda.

Sanarwar mai ɗauke da sa hannun Manjo Janar Edward Buba ta ƙara da cewa mayaƙan Boko Haram 104 da su da iyalansu duk sun miƙa wuya ga sojoji, sannan an kuma kama mutum 22 da kitsa satar ɗanyen man fetur.

More News

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...

Sojojin Najeriya Sun Musanta Jita-jitar Mutuwar Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja

Daga Sabiu AbdullahiRundunar Sojojin Najeriya ta karyata rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja,...