Sojojin Najeriya sun yi mummunar ta’asa wa ƴan bindiga a Kaduna

Dakarun Sojojin Najeriya sun yi nasarar halaka ‘yan bindiga shida da ke addabar mazauna karamar hukumar Birnin-Gwari ta jihar Kaduna.

Mukaddashin daraktan hulda da jama’a na rundunar soji ta daya, Laftanar Kanar Musa Yahaya, ya ce ‘yan bindigar sun haɗu da ajalin nasu ne a ranar Alhamis lokacin da sojojin da ke aiki da sahihan bayanan sirri suka kai wani samame a kauyukansu a Sabon Birnin, Dogon Dawa, Saulwa, Maidaro- Ngede Allah da Kidenda duk a karamar hukumar Birnin-Gwari.

Ya bayyana cewa sojojin sun taɓo ‘yan ta’addan inda nan take suka yi artabu da su har suka kashe shida daga cikinsu.

Sojojin, a cewar kakakin rundunar, sun kuma kwato bindigogin AK-47 guda biyu, da gidan albirushin AK-47 guda hudu, harsashi guda goma sha hudu na 7.62mm, rigunan ‘yan fashi guda arba’in, da kuma babura tara.

More News

Kotu ta sauke kakakin majalisar Nasarawa

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke zamanta a Abuja ta kori kakakin majalisar dokokin jihar Nasarawa, Rt. Hon. Ibrahim Balarabe Abdullahi dan jam’iyyar...

Masu cin gajiyar shirin Npower na kokawa game da rashin biyansu

Wasu masu cin gajiyar shirin gwamnatin tarayya na N-Power a ranar Litinin sun koka kan yadda ake ci gaba da biyan su alawus-alawus din...

Tinubu ya sake naɗa Mele Kyari a matsayin shugaban NNPCL

Shugaba Bola Tinubu ya sake nada Malam Mele Kyari a matsayin babban jami’in gudanarwa na kamfanin man fetur na kasa (NNPCL). An bayyana hakan ne...

Ba baƙon abu ba ne don an haifi yaro da haƙori a bakinsa—in ji masana lafiyar yara

Likitocin kula da lafiyar yara sun ce jariran da ke da hakora daya ko biyu a lokacin haihuwa hakan ba baƙon al'amari ba ne. Wannan...