Sojojin Najeriya Sun Musanta Jita-jitar Mutuwar Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja

Daga Sabiu Abdullahi

Rundunar Sojojin Najeriya ta karyata rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja, ya rasu.

Jita-jitar ta samo asali daga wani ɗan jarida da ya yi ikirarin cewa Lagbaja ya mutu sakamakon ciwon daji a mataki na uku a wani asibiti a ƙasar waje.

Duk da haka, majiyoyi daga hedkwatar sojoji sun tabbatar da cewa Lagbaja bai rasu ba, sai dai yana fama da matsanancin rashin lafiya. An bayyana cewa yana ƙasar waje don neman magani.

Sojojin Najeriya sun bayyana wannan jita-jita a matsayin “ƙarya”, duk da cewa ba a samu damar jin ta bakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Sojojin, Manjo Janar Onyema Nwachukwu, ba a lokacin.

More News

An kashe shugaban wata makaranta a Abuja a cikin gidansa

Wasu mutane da kawo yanzu ba a san ko su waye ba sun kashe, Bala Tsoho Musa shugaban makarantar Abuja Rehabilitation Centre. Musa wanda aka...

Gwamnan Jigawa ya dakatar da kwamishinan da ake zargi da lalata da matar aure

Gwamnan jihar Jigawa, Umar Namadi ya dakatar da Auwal  Danladi Sankara kwamishinan ayyuka na musamman na jihar kan zargin da ake masa na lalata...

APC ta lashe zaben kujerun ƙananan hukumomi da kansilolin jihar Kaduna

Jam'iyyar APC ta lashe zaben dukkanin kujerun ƙananan hukumomin jihar Kaduna 23 da kuma na kejerun kansilolin jihar. Hajara Muhammad shugabar hukumar zaɓe mai zaman...

Tinubu ya dawo gida Najeriya daga Birtaniya

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo gida Najeriya bayan da ya shafe mako biyu yana hutu a Birtaniya. Shugaban ƙasar ya sauka a filin...