Rundunar sojan Najeriya ta ce dakarunta da ke aiki a rundunoni daban-daban sun yi nasarar kashe waɗanda ta kira ‘yan ta’adda fiye da 100 a arewacin ƙasar.
Rundunar ta bayyana haka ne ta bakin kakakinta Benard Onyeuko a yau Alhamis yayin wani taron manema labarai, yana mai cewa sun cimma nasarar ce cikin mako biyu da suka gabata.
Cikin ayyukan da ta ce rundunarta ta Operation Hadarin Daji na gudanarwa a jihohin arewa maso yamma, sojoji sun yi nasarar kashe ‘yan fashin daji 90 tare da ƙwato shanu 574 da babur 22 da kuma bindigogi ƙirar AK-47 uku a Jihar Zamfara.
Su ma dakarun Operation Hadin Kai a yankin arewa maso gabas sun harbe wasu ‘yan ƙungiyar Boko Haram ko kuma ISWAP 10 a Jihar Borno. Sojojin sun ƙwace kekuna 10 da wasu bindigogi daga hannun masu iƙirarin jihadin.
Sai kuma rundunar Whirle Stroke da ta kashe wani “ƙasurgumin” ɗan fashi mai suna Janta a Ƙaramar Hukumar Katsina Ala ta JIhar Benue.