Sojoji sun yi ikirarin hambarar da gwamnatin Bazoum a Nijar

Sojoji sun yi ikirarin hambarar da gwamnatin Nijar bayan wani juyin mulkin da aka yi a yammacin Afirka ranar Laraba lokacin da jami’an tsaron fadar shugaban kasar suka tsare shugaba Mohamed Bazoum.

Majiyar fadar shugaban kasar ta bayyana cewa, mambobin masu gadin shugaban kasar sun rufe kofar shiga gidan shugaban da ofisoshinsu da ke Yamai babban birnin kasar, kuma bayan da tattaunawar ta tsaya, “sun ki sakinsa”.

Sojojin sun ce za a dakatar da “dukkan cibiyoyi” a kasar, a rufe kan iyakoki da kuma sanya dokar ta-baci “har sai an samu sanarwa” daga karfe 10 na dare zuwa 5 na safe.

“Mu da jami’an tsaro… mun yanke shawarar kawo karshen mulkin shugaba Bazoum,” in ji Kanar-Manjo Amadou Abdramane a wani jawabi da ya yi ta gidan talabijin da yammacin Laraba.

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...