Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na man fetur da dangoginsa a yankin Neja Delta.

A wata sanarwa ranar Litinin, Danjuma Jonah mataimakin daraktan yaÉ—a labarai na  rundunar ya ce an kama mutane da dama da ake zargi da hannu a lamarin.

Jonah ya ce jiragen ruwa  54 ƙirar gida da kuma motoci da ake amfani da su wajen jigilar man aka ƙwace.

Ya ce an samu wannan gagarumar nasara ne a samame da kuma farmakin da rundunar ke cigaba da kaiwa jihohin dake yankin.

More News

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...

Sojojin Najeriya Sun Musanta Jita-jitar Mutuwar Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja

Daga Sabiu AbdullahiRundunar Sojojin Najeriya ta karyata rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja,...

An kashe shugaban wata makaranta a Abuja a cikin gidansa

Wasu mutane da kawo yanzu ba a san ko su waye ba sun kashe, Bala Tsoho Musa shugaban makarantar Abuja Rehabilitation Centre. Musa wanda aka...