
Dakarun sojan Najeriya da suka fito daga Birged ta 7 kuma suke aiki da rundunar Operation Fansan Yamma sun kashe yan fashin daji takwas a jihar Katsina.
Yan ta’addar sun bakunci lahira ne a wata musayar wuta da suka yi da dakarun sojan a ranar Laraba akan hanyar Kurfi zuwa Batsari.
Daraktan yada labarai na fannin tsaro, Manjo Janar Markus Kangye ne ya bayyana haka a ranar Alhamis a cikin wata sanarwa da ya fitar.
Kangye ya ce sojojin sun hanzarta bude wuta kan yan bindigar inda suka dakile shirinsu bayan daukan tsawon lokaci ana musayar wuta.
Ya ce yan ta’addar sun kwashi kashinsu a hannu inda aka gano bindigar AK-47 guda biyar gidan zuba harshin AK-47 guda 6 sai harsashi na musamman mai tsayin 7.62mm guda 13.
A cewarsa soja guda daya ya jikkata inda yake can asibiti yana samun kulawar likitoci.
Ya kara da cewa ma’aikatar tsaro ta Najeriya ta yabawa sojojin kan kwarewa da kuma jarumtaka da suka nuna.