
Dakarun rundunar sojan Najeriya dake aiki da rundunar Operation Fansar Yamma wacce ke aikikin samar da tsaro a jihohin yankin arewa maso yamma sun samu nasarar kashe yan bindiga 10 a wani mummunan hari da su kai kan maboyar yan bindingar.
Dakarun sun kai farmaki ne a maboyar yan bindingar dake kauyukan Mai Tashi da kuma Danjibga a karamar hukumar Gusau ta jihar Zamfara da kuma kauyen Munhaye a karamar hukumar Tsafe ta jihar ranar 9 ga watan Yuni.
Baburan hawa 5 da kuma bindinga da alburasai dakarun su ka kwace a hannun yan ta’addar.
Bayanin nasarar da rundunar sojan ta samu na kunshe ne a cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a shafin ta na Facebook.