Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 5 tare da lalata sansaninsu 4 a Borno

Sojojin rundunar kasa da kasa dake samar da tsaro a yankin tafkin Chadi sun kashe mayaƙa 6 na ƙungiyar ƴan ta’adda ta ISWAP a jihar Borno.

Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi shi ne ya bayyana haka inda ya ce an kai farmakin ne kan ƴan ta’addar da haɗin gwiwar rundunar samar da tsaro ta Operation Hadin Kai.

Zagazola ya bayyana cewa sojoji sun kaddamar da farmaki kan maboyar yan ta’addar a ranar 4 ga watan Disamba.

Wata majiyar jami’an sojan leƙen asiri ta bayyana cewa sojojin sun tarwatsa sansanonin ƴan ta’addar guda huɗu dake kauyukan Ngurnoa, Gumnari, Naira da Amburam a ƙaramar hukumar Monguno ta jihar Borno.

Majiyar ta ce sojoji sun yi musayar wuta da ƴan ta’addar abun da ya tilasta musu tserewa ta cikin ruwa har ta kai ga an kashe biyar daga cikin su.

Ɗaya daga cikin jami’an sojojin da suka kai farmaki ya samu rauni kuma tuni aka ɗauko a jirgin sama ya zuwa asibitin sojoji dake Maiduguri.

Sojojin sun gano bindiga kirar GPMG gidan saka harsashi na bindigar AK-47 guda a cikin wani bangare na ruwan da bashi da zurfi

More News

Tinibu ya aikawa da majalisar dattawa sunaye 7 na  ministocin da zai naɗa

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi kira ga majalisar dattawa da ta tabbatar da sunayen mutane 7 da ya tura majalisar da zai...

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...