Sojoji Sun Kashe Gawurtaccen Ɗan Bindiga Boderi

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun kashe wasu gawurtattun masu garkuwa da mutane da suka jima suna addabar al’umma.

Mai magana da yawun rundunar sojan Najeriya, Onyeama Nwachukwu shi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis .

Ya ce ƴan fashin daji shida aka kashe a yayin farmakin da aka kai a yankin Bada-Riyawa dake kan hanyar Birnin Gwari zuwa Kaduna a ranar 22 ga watan Faburairu.

Ya ce bayanan sirri sun bayyana cewa Boderi da Bodejo  gawurtattun masu garkuwa da mutane na daga cikin yan fashin dajin da aka kashe a yayin arangamar.

Mutanen biyu sune ke da alhakin kai hari kan makarantar sojoji ta NDA,  kwalejin aikin gona dake Afaka, jami’ar Greenfield da kuma makarantar ƴan mata ta Yauri.

Baderi ya shafe shekaru da dama yana addabar al’umma kana ana zarginsa da haɗa baki da ƴan ta’adda domin kafa masu sansani a dazukan dake yankunan da yake da iko da su.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...