Sojoji sun kashe ɗan bindiga a Kaduna

Rundunar sojan Najeriya ta ce dakarunta sun kashe yan bindiga da kuma gano bindigar AK-47 ɗaya a Kaduna.

Jami’an sojojin rundunar shiya ta ɗaya ne suka kai farmakin a kananan hukumomin Chikun da Kajuru.

Musa Yahaya mai rikon muƙamin jami’in hulɗa da jama’a na rundunar sojan Najeriya shiya ta ɗaya shi ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa ranar Laraba.

Ya ce sojojin bisa dogaro da bayanan sirri sun yi kwanton ɓauna a kan hanyar da ƴan bindigar suke bi a titin Kwant-Kabai-Kubusu a ranar Laraba.

Yahaya ya ce farmakin wani bangare ne na ƙoƙarin da rundunar take na raba jihar da ƴan ta’ada, ƴan bindiga da kuma sauran batagari dake dazukan jihar.

Ya ce a yayin farmakin a musayar wutar da aka yi ɗan bindiga guda ya rasa ransa yayin da sauran suka tsere da raunin harbin bindiga.

“bindigar AK-47 guda ɗaya, gidan harsashi ɗaya, maganin dabbobi da kuma kayan sawa su ne aka gano” a cewar sanarwar.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...