Sojoji sun kashe ƴan ta’adda biyu tare da gano makamai a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun kashe wasu ƴan ta’adda biyu a ƙauyen Kana dake ƙaramar hukumar Biu ta jihar Borno.

A wata sanarwa ranar Asabar rundunar sojan ta ce an kashe ƴan ta’addar ne a ranar 19 ga watan Afrilu.

Rundunar sojan ta ce dakarunta sun yi arangama da ƴan ta’addar a wajejen ƙauyen Nguma ta kara da cewa an gano babur ɗaya da kekuna 6 sai bindiga ƙirar AK-47 da kuma sauran kayayyaki da aka yi watsi da su.

A kuma wani samamen na daban dakarun sojan na Najeriya sun kai samame a ƙauyen Abuni dake ƙaramar hukumar Awe ta jihar Nasarawa kan wasu maɓoyar bata gari inda aka gano bindigogi.

An samu nasarar gano bindigogi biyu ƙirar AK-47 a gidan wani da ake kira Abdullahi Musa tare da kama ƙarin wasu mutane.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...