Dakarun runduna ta 1 ta sojin Najeriya sun kashe ‘yan ta’adda 14 tare da kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su a wani samame na baya-bayan nan a jihohin Neja da Kaduna, kamar yadda rundunar ta sanar a ranar Lahadi.
A wata sanarwa a dandalin X, mai magana da yawun rundunar Laftanar Kanar Musa Yahaya ya ce sojojin sun fatattaki ‘yan ta’addan daga maboyarsu, inda suka yi nasarar kwato muggan makamai tare da kubutar da wadanda suka yi garkuwa da su.
“A ranar Asabar a Jihar Neja, sojoji sun yi artabu da ‘yan ta’adda a kauyen Madawaki, inda suka kashe biyu tare da tilasta wa wasu tserewa. Sun kwato bindigogi kirar AK-47, alburusai, da babur.
“A sansanin da aka kashe jagoran ‘yan ta’addar Ali Kachalla, sojoji sun ceto maza 13 da aka yi garkuwa da su a watan Oktoba. Sun kuma gano fasfo mai alaka da wata babbar kungiyar ta’addanci.
“Bincike a sansanin ya kai ga ceto mutane 13 da aka yi garkuwa da su, dukkansu maza. An bayyana cewa an sace mutanen ne a jihar Neja a ranar 13 ga Oktoba, 2023.
“Abubuwan da aka kwato daga sansanin sun hada da fasfo na kasa da kasa da ake zargin na da wata babbar alaka ne da masu tayar da kayar baya,” in ji sanarwar.