Sojoji sun dakile harin mayakan ISWAP a garin Monguno

Jami’an rundunar sojan Najeriya sun samu nasarar dakile wani hari da mayakan kungiyar ISWAP suka yi kokarin kai wa a karamar hukumar Monguno ta jihar Borno.

Zagazola Makama masani dake wallafa rubutu kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi ya ce sojojin shiya ta 3 na rundunar kasa da kasa wato MNJTF su ne su ka yi artabu da yan ta’addar.

Makama ya ce yan ta’addar sun farma yankin a cikin motocin Hilux da dama da aka girkawa bindigar harbo jirgi a saman su a ranar Alhamis.

Bayanan da ya wallafa sun bayyana cewa wasu daga cikin yan ta’addar sun zo akan babura a yayin da wadanda su ke a kafa suka farma sojojin dake Charlie 6 a cikin garin Monguno.

A karshe dai yan ta’addar sun tsere.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...