Sojoji sun kai farmaki wa ƴan bindiga a Kaduna

‘Yan bindiga a maboyarsu da ke kewayen Kagarko, Iche, Taka-Lafiya Gidan Makeri da Jangala a Jihar Kaduna an ce sun tsere bayan da sojoji sama da 100 suka mamaye dajin karamar hukumar Kagarko.

Al’ummomi da dama a masarautar Kagarko sun sha fama da hare-haren ‘yan bindiga da suka yi awon gaba da mazauna yankin da manoma, lamarin da ya sa jama’a suka kasa jurewa.

Bayan isowar sojojin da suka kai farmaki maboyarsu da wasu al’ummomin karkara tare da kame wasu da ake zargin masu ba da labari, an shawo kan lamarin, kuma an samu zaman lafiya a yankin.

Wani mai rike da sarautar gargajiya a garin Kagarko, Suleiman Aliyu, ya ce sojojin da suka shiga garin Kagarko da misalin karfe 11 na safiyar ranar Laraba a cikin motocin Hilux da manyan motoci da babura, sun zarce zuwa kauyukan Iche, Taka-Lafiya, Gidan Makeri da Janjala da ke kusa da dajin, don farautar ‘yan fashi.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...