Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami’ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da su a, Zamfara.
Wasu dalibai da ba a san yawansu ba ne aka bada rahoton yan bindiga sun sace daga gidajen kwanansu dake Sabon Gida a karamar hukumar Bungudu ta jihar Zamfara.
A wata sanarwa, Sulaiman Idris babban mataimaki na musamman kan kafafen yaɗa labarai ga gwamnan Zamafara ya ce sojojin sun kuma kashe da yawa daga cikin yan bindigar a musayar wuta.
Idris ya ce gwamnan jihar Dauda Lawal Dare ya kirawo taron dukkanin hukumomin tsaro domin tattauna batun sace mutanen.