Sojoji sun ceto mutane 24 da aka yi garkuwa da su a Zamfara

Sojojin rundunar Operation Hadarin Daji sun samun nasarar ceto wasu mutane 24 da yan bindiga suka yi garkuwa da su a karamar hukumar Maru ta jihar Zamfara.

Sojojin sun samu nasarar ceto mutanen ne biyo bayan bayanan sirri da suka samu kan wata maboyar yan bindiga dake dajin Kabugu Lamba.

A cewar rahotanni sojojin sun yi musayar wuta da yan bindigar abin da ya tilasta musu tserewa da kafafunsu tare da barin wadanda suke garkuwar da su.

Yan bindiga hudu ne suka mutu a yayin arangama da sojojin yayin da sauran suka gudu da raunin harbin bindiga

Mutanen da aka kubutar sun haɗa da maza 14 jariri 1 da kuma mata 9 da tuni aka miƙa su ga hukumomin da ya dace domin haɗa su da iyalinsu.

More News

Tinibu ya aikawa da majalisar dattawa sunaye 7 na  ministocin da zai naÉ—a

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi kira ga majalisar dattawa da ta tabbatar da sunayen mutane 7 da ya tura majalisar da zai...

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...