Sojoji Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

Rundunar Sojan Najeriya ta ce dakarunta sun ceto mutane 16 da ƴan bindiga suka yi garkuwa da su daga ƙauyen Tantatu a ƙaramar hukumar Kajuru ta jihar Kaduna.

A ranar Lahadi ne Æ´an fashin daji su ka farma garin na Tantatu da misalin Æ™arfe 10 na dare inda suka farfasa shaguna suka sace kayan abinci da kuma sauran kayayyaki a gidajen jama’a.

Aƙalla mutanen garin 87 aka ce maharan sun ɗauke a yayin farmakin.

Ko da a ranar Asabar ma mutane 14 aka bada rahoton an sace a ƙauyen Dogon Nama dake ƙaramar hukumar ta Kajuru.

A wata sanarwa ranar Litinin, Onyeama Nwachukwu mai magana da yawun Rundunar Sojan Najeriya ya ce sojojin sun amsa kiran da aka yi musu bayan da aka kai hari garin ranar Lahadi da da daddare.

Nwachukwu ya ce sojojin sun yi musayar wuta da Æ´an bindigar har ta kai ga an samu nasarar ceto mutanen.

Ya ƙara da cewa sojojin na cigaba da bincike cikin dajin a ƙoƙarin ceto ƙarin wasu mutanen.

More News

Gwamnatin Adamawa Ta Ƙara Hutun Ɗaliban Makarantu Saboda Annobar Cutar Ƙyanda

Gwamnatin jihar Adamawa ta tsawaita lokacin komawar É—aliban jihar makarantunsu domin fara  zangon karatu na uku saboda annobar cutar Æ™yanda. A wata sanarwa ranar Litinin,...

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen ÆŠan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen É—an fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...