Sojoji Sun Ceto Ma’aikatan Agaji Biyu A Borno

Sojojin Najeriya dake aiki a bataliya ta 51 dake Banki sun kashe mayakan Boko Haram da dama a jihar Borno.

A cewar Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan harkar tsaro a yankin tafkin Chadi an kai farmakin ne a ranar Juma’a tare da haÉ—in gwiwar jami’an tsaron Civilian JTF.

Bayanan da aka wallafa sun bayyana cewa sojojin sun kai farmaki ne a maboyar yan ta’addan dake Gargash a karamar hukumar Bama ta jihar.

An jiyo wata majiya dake randunar sojan Najeriya na cewa yan ta’addar na shirin kai hari ne lokacin da sojoji suka kashe su.

Ma’aikatan agaji biyu da aka sace a Monguno a cikin shekarar 2022 aka ceto a yayin artabun da aka yi da yan ta’addan.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Wani mutumi ya kashe mahaifiyarsa a kan kudi

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun kama wani mazaunin kauyen Kajola da ke kusa da Apomu a jihar mai suna Lukman Adejoju bisa...

Mayaƙan Boko Haram Biyu Sun Miƙa Kansu Ga Sojoji

Rundunar dakarun soja ta ƙasa da ƙasa wato Multi National Task Force(MNJTF) a turance shiya ta 3 dake Monguno a Najeriya ta bayar da...

Sojoji a birnin Ibadan  sun kama Æ´an fafutukar kafa Æ™asar Oduduwa

Dakarun rundunar sojan Najeriya  sun samu nasarar kama wasu mutane masu fafutukar kafa ƙasar Oduduwa a birnin Ibadan na jihar Oyo. Masu fafutukar sanye da...