Sojoji a Lagos sun kama wanda ake zargi da kashe shugaban Fulani a jihar Filato

Rundunar sojan Najeriya ta ce dakarunta sun kama Philip Gokas wanda ake zargi da kisan Adamu Gabdo wani shugaban al’ummar Fulani a jihar Filato.

A ranar 23 ga watan Satumba ne aka kashe Gabdo wanda shi ne ArÉ—on Fulani na Panyam dake karamar hukumar Mangu ta jihar Plateau.

Kwanaki bayan kisan, Taoreed Lagbaja babban hafsan sojan Najeriya ya bawa jami’an rundunar samar da tsaro a jihar Plateau ta Operation Safe Haven da su kamo wanda suka kashe Gabdo.

A wata sanarwa ranar Laraba rundunar sojan Najeriya ta ce jami’an rundunar Opera Safe Haven sun gano wanda ake zargi a yankin Ogba dake jihar Lagos bayan shafe makonni suna farautarsa.

A cewar sanarwar an kama Gokas ne yana shan giya a wani wurin kallon wasan kwallon kafa.

Rundunar sojan ta ce wanda ake zargi ya amsa laifin kisan Gabdo.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...