
Bankin Raya Kasashen Afrika AFDB ya zabi, Sidi Ould Tah dan kasar Mauritania a matsayin sabon shugaban bankin.
An zabi Tah ranar Alhamis a wurin taron bankin na shekara-shekara da aka gudanar a hedkwatar bankin dake birnin Abidjan na kasar Kodebuwa.
Sabon shugaban zai maye gurbin, Akinwunmi Adesina dan Najeriya wanda ya shafe shekaru 10 yana jagorantar bankin tun bayan da aka zabe shi a shekarar 2015.
Sanarwar ta ce Tah zai kama aiki a ranar 1 ga watan Satumba a matsayin shugaban bankin na 9.
Tah ya samu nasara ne a cikin mutane 5 da suka nun sha’awarsu ta jagorantar ragamar bankin.
Sauran mutanen da suka nemi shugabancin sun hada da Amadou Hott (Senegal), Samuel Maimbo (Zambia), Mahamat Abbas Tolli (Chad), da Bajabulile Swazi Tshabalala (Afrika ta Kudu).