Shugabar matan jam’iyar NNPP ta Shiyar Arewa Maso Yamma, Aisha Ahmad Kaita ta sauka daga muÆ™aminta.
A’isha wacce ta sanar da sauka daga muÆ™aminta  a yayin wani taron manema labarai a Kano ranar Talata ta ce ta sauka daga muÆ™aminta ne a Æ™ashin kanta kuma za ta cigaba da zama a jam’iyar ta NNPP.
Ta ƙara da cewa matakin da ta ɗauka na da alaƙa kan yadda aka ƙi bawa mutanenta muƙami a gwamnatin Kano tun bayan da aka kafa gwamnatin.
Ta kuma bayyana biyayya ta ga jagoran jam’iyar, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.
A Æ´an kwanakin nan dai Æ´aÆ´an jam’iyar ta NNPP na cigaba da nuna rashin jin daÉ—insu kan yadda aka yi watsi da su tun bayan kafa gwamnati.