Shugabannin Turai Sun Yi Watsi da Buƙatar Trump Kan Tsaron Mashigin Hormuz


Wasu ƙarin shugabannin ƙasashen Turai sun yi watsi da buƙatar Shugaban Amurka, Donald Trump, na neman taimako wajen tabbatar da tsaron zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigin Hormuz, bayan Iran ta rufe yankin.

Bayan wani taron ministocin harkokin wajen Tarayyar Turai, babbar jami’ar kula da manufofin ƙasashen waje na ƙungiyar, Kaja Kallas, ta ce “babu wanda ke son yin hakan,” inda ta ƙara da cewa “Wannan ba yaƙi ne na ƙasashen Turai ba”.

Shi ma shugaban Finland, Alexander Stubb, ya shaida manema labarai cewa Mista Trump ne da kansa ya yanke shawarar fara yaƙi da Iran ba tare da tuntuɓar wasu ba, don haka ya kamata ya nemo mafita da kansa.

Shugaban gwamnatin Jamus, Friedrick Merz, ya bayyana cewa rikicin Iran ba batu ne da ya shafi ƙungiyar NATO ba. Haka kuma, mahukunta a birnin Paris sun fito fili sun shaida wa Trump cewa ba za su tura dakarunsu zuwa mashigin Hormuz ba.

Tun da farko a Fadar White House, Shugaba Trump ya soki wasu ƙasashen duniya, yana mai cewa sun yi shiru kan matakin da ya ɗauka.

More from this stream

Recomended