Shugabannin kungiyar ƙwadago za su tattauna da mambobinsu bayan ganawar da su ka yi da gwamnati.

Shugabannin kungiyoyin ƙwadago na NLC da TUC sun amince su tattauna da mambobinsu bayan ganawar da suka yi da tawagar gwamnatin tarayya a ranar Laraba kan yajin aikin da ake yi.

Taron ganawar ya gudana ne a ofishin mai bawa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu dake Abuja domin lalubo mafita kan yajin aikin.

Ma’aikatan sun tsunduma yajin aiki a ranar 14 ga watan Nuwamba domin nuna rashin amincewarsu kan yadda aka ci zarafin Joe Ajaero shugaban kungiyar kwadago ta NLC a jihar Imo.

Kungiyar ta yi zargin cewa kawo yanzu babu wanda aka kama ballantana gurfanar da su gaban kotu kan batun.

Sai dai a wata sanarwa da ya fitar kan yajin aikin mai bawa shugaban ƙasar shawara kan sha’anin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce tuni aka kama wasu da ake zargin suna da hannu kan lamarin.

Taron ganawar da aka yi ya samu halartar ministan ƙwadago Simon Lalong da kuma karamar ninistar ma’aikatar, Nkeiruka Onyeajeocha.

Da yake magana bayan zaman da aka yi shugaban kungiyar TUC ya ce sun tattauna sosai da tawagar gwamnatin tarayya.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...