Shugaban Burundi ya nemi a fara jefe ƴan luwaɗi a ƙasar

Shugaban kasar Burundi, Evariste Ndayishimiye, ya nuna ƙyamarsa ga ‘yan luwadi a ranar Juma’a, yana mai cewa ya kamata a riƙa jefe ma’auratan jinsi daya a bainar jama’a.

Har ila yau ya caccaki kasashen yammacin duniya da ke matsa wa wasu kasashe su ba dama wa ‘yan luwadi ko kuma su rasa taimako.

Luwaɗi a Burundi, watau kasar Kirista masu ra’ayin mazan jiya a gabashin Afirka, laifi me da tun shekara ta 2009 aka yanke masa hukuncin daurin shekaru biyu a gidan yari.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]