Shugaba Tinubu yana ganawa da gwamnonin jam’iyyar APC

A halin yanzu dai shugaba Bola Tinubu yana ganawa da gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki a karkashin inuwar jam’iyyar Progressive Governors Forum (PGF).

Shugaban PGF, wanda kuma shi ne gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma, ya jagoranci wasu takwarorinsa goma sha hudu zuwa taron.

Sauran gwamnonin sun hada da na Kwara, Benue, Kaduna, Ekiti, Cross River, Ogun, Borno, Yobe, Kebbi, Jigawa, Ondo, Kogi, da Sokoto, sun halarci taron.

Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, wanda kotun koli ta tabbatar da nasarar zabensa a yau, bai halarci taron ba.

Taron yana gudana ne a zauren majalisar zartarwa na fadar shugaban kasa.

Ba a san ajanda taron ba har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu É—aliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karÉ“ar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...