Shugaba Tinubu yana ganawa da gwamnonin jam’iyyar APC

A halin yanzu dai shugaba Bola Tinubu yana ganawa da gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki a karkashin inuwar jam’iyyar Progressive Governors Forum (PGF).

Shugaban PGF, wanda kuma shi ne gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma, ya jagoranci wasu takwarorinsa goma sha hudu zuwa taron.

Sauran gwamnonin sun hada da na Kwara, Benue, Kaduna, Ekiti, Cross River, Ogun, Borno, Yobe, Kebbi, Jigawa, Ondo, Kogi, da Sokoto, sun halarci taron.

Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, wanda kotun koli ta tabbatar da nasarar zabensa a yau, bai halarci taron ba.

Taron yana gudana ne a zauren majalisar zartarwa na fadar shugaban kasa.

Ba a san ajanda taron ba har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]