Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya sauka a birnin Makurdi, babban birnin Jihar Benue, yayin da ake ci gaba da nuna damuwa kan hare-haren da suka faru a jihar kwanan nan, wadanda suka yi sanadiyyar salwantar rayuka da dama.
Rahotanni sun tabbatar da cewa shugaban ya isa filin jirgin sama na Makurdi, wanda ke cikin sansanin rundunar sojin saman Najeriya na Tactical Air Command, da misalin ƙarfe 12:58 na rana a ranar Talata.
Ziyarar ta biyo bayan kisan gillar da aka yi a garin Yelwata, da ke ƙaramar hukumar Guma, lamarin da ya tayar da ƙura a fadin ƙasar nan.
Shugaba Tinubu zai gana da muhimman jiga-jigan siyasa da na al’umma a jihar domin tattauna hanyoyin shawo kan matsalolin tsaro da suka addabi yankin.
A halin yanzu dai, ana sa ran za a fitar da ƙarin bayani kan tafiyar shugaban a sa’o’i masu zuwa.
Shugaba Tinubu Ya Isa Benue Bayan Munanan Hare-haren Da Suka Yi Sanadin Mutuwar Ɗaruruwan Mutane
