Shugaba Tinubu ba ya daukar lamarin tsaron Najeriya da wasa—Kashim Shettima

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya ce Shugaban kasa Bola Tinubu ba ya daukar lamarin kalubalen tsaron kasar da wasa.

Shettima ya bayyana haka ne a ranar Litinin yayin da yake karbar shugabannin Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya a fadar shugaban kasa.

“Halin tsaro a kasar wani abu ne da shugaban kasa ke matukar sha’awar shi kuma baya daukarsa da wasa,” in ji mataimakin shugaban kasar a wata sanarwa da kakakinsa Stanley Nkwocha ya fitar.

“Laccar kasa da kasa da NAN ke shiryawa ya dace sosai, musamman kan batun rashin tsaro a yankin Sahel.”

Ya yi kira da a yi kokari na shiyya-shiyya da na gamayya don magance matsalar rashin tsaro a yankin Sahel na yammacin Afirka, duba da yadda yanayin tsaro a yankin Sahel ke da matukar tasiri ga Najeriya da kuma kasashen da ke makwabtaka da ita.

More from this stream

Recomended