Shin Yaushe Za’a Bude Sufurin Jiragen Kasa-da-Kasa a Najeriya?

Hukumar kula da filayen jiragen saman Najeriya NCAA, ta bayyana cewa za ta kara wa’adin bude sashen tashi da saukan jirage na kasa-da-ka a filayen jiragen sama har zuwa 19 ga watan Oktoba, a maimokon 19 ga watan Augustar da ta bayyana a baya.

Adamu Abdullahi, darakta a hukumar ta NCAA ne ya bayyana wannan matakin a wata hirar da yayi da jaridar BusinessDay.

Abdullahi ya ce ba za’a fara zirga-zirgar jiragen sama na kasa-da-kasa ba har sai nan da watan Oktoba.

“Idan mun sauya matsayarmu, za mu bayyana sabon hukuncin da mu ka dauka,” in ji Abdullahi.

Hakan na nufin cewa jirage masu aiki na musamman da na jami’an difilomasiyya ne kadai aka baiwa dama a halin yanzu, har sai an tabbatar da lokacin bude zirga-zirgar kasa-da-kasa.

A cikin watan Maris din da ya gabata ne gwamnatin Najeriya ta dakatar da zirga-zirgar jiragen kasa-da-kasa domin dakile yaduwar cutar Coronavirus.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

ÆŠan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...