Shin Yaushe Za’a Bude Sufurin Jiragen Kasa-da-Kasa a Najeriya?

Hukumar kula da filayen jiragen saman Najeriya NCAA, ta bayyana cewa za ta kara wa’adin bude sashen tashi da saukan jirage na kasa-da-ka a filayen jiragen sama har zuwa 19 ga watan Oktoba, a maimokon 19 ga watan Augustar da ta bayyana a baya.

Adamu Abdullahi, darakta a hukumar ta NCAA ne ya bayyana wannan matakin a wata hirar da yayi da jaridar BusinessDay.

Abdullahi ya ce ba za’a fara zirga-zirgar jiragen sama na kasa-da-kasa ba har sai nan da watan Oktoba.

“Idan mun sauya matsayarmu, za mu bayyana sabon hukuncin da mu ka dauka,” in ji Abdullahi.

Hakan na nufin cewa jirage masu aiki na musamman da na jami’an difilomasiyya ne kadai aka baiwa dama a halin yanzu, har sai an tabbatar da lokacin bude zirga-zirgar kasa-da-kasa.

A cikin watan Maris din da ya gabata ne gwamnatin Najeriya ta dakatar da zirga-zirgar jiragen kasa-da-kasa domin dakile yaduwar cutar Coronavirus.

More News

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...