Shettima Ya Kai Ziyarar Jaje da Ta’aziyya Jihar Kaduna

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya kai ziyarar jaje da ta’aziyya jihar Kaduna na mutanen da harin jirgin sojoji ya kashe a Æ™auyen Tudun Biri dake jihar.

Shettima ya sauka a filin jirgin saman sojan Najeriya dake Kaduna.

A yayin ziyarar mataimakin shugaban kasar yana tare da shugaban majalisar wakilai ta tarayya, Tajuddeen Abbas da kuma shugaban jam’iyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje.

Gwamnan jihar Kaduna, Mallam Uba Sani shi ne ya tarbi mataimakin shugaban ƙasar a filin jirgin.

A ranar Lahadi ne wani jirgin sama marar matuki na rundunar sojan Najeriya ya saki bam kan wasu mutane da suke gudanar da taron Maulidi a ƙauyen Tudun Biri dake ƙaramar hukumar Igabi ta jihar Kaduna.

Kawo yanzu dai mutane sama da 100 ne aka tabbatar da mutuwar su a yayin sama da mutane 60 suka jikkata a harin.

More News

Tinibu ya aikawa da majalisar dattawa sunaye 7 na  ministocin da zai naÉ—a

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi kira ga majalisar dattawa da ta tabbatar da sunayen mutane 7 da ya tura majalisar da zai...

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...