Shehun Borno ya bukaci komawa ga Ubangiji saboda ƙarancin ruwan sama

Shehun Borno, Alhaji (Dr) Abubakar Ibn Umar Garbai El-Kanemi, ya yi kira da a dage da addu’a domin Allah ya kawo dauki kan karancin ruwan sama a wasu sassan jihar Borno.

Hakan na kunshe ne a cikin wata takarda mai dauke da sa hannun Zanna Laisu Kazalma, Sakataren Majalisar Masarautar Borno, Shehun Borno ya yi kira ga dukkan Limamai da su ba da addu’o’i na musamman daga ranar Juma’a, 21 ga Yuli, 2023 don neman taimakon Allah Ta’ala.

Shehu ya umurci dukkan hakimai da ƙauye a fadin jihar da su hada kan al’ummar Musulmi a yankunansu domin kai dauki ga mabuƙata, marayu da nakasassu.

Ya kuma shawarci iyaye da su rika yi wa ’yan uwa nasiha kan su guji dabi’u na fasikanci, munanan dabi’u, da shaye-shayen miyagun kwayoyi.

Sannan ya bukaci daukacin ‘yan kasuwa da su ji tsoron Allah wajen gudanar da sana’arsu ta halal.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...