Sevilla: Sarakan gasar Europa League sun sake lashe ta a karo na shida

Sevilla

Bayanan hoto,
Babu ƙungiyar da ta lashe gasar sau huɗu sai Sevilla mai guda shida

Sarakan Gasar Europa League – Sevilla – sun sake lashe gasar a karo na shida bayan sun lallasa Inter Milan da ci 3-2 a birnin Cologne na Jamus a daren Juma’a.

Sevilla ta sake kafa tarihin lashe kofin fiye da kowacce ƙungiya a Turai, inda Inter Milan ke biye mata da guda uku.

Wasa ya ɗauki ɗumi ne bayan ɗan wasan bayan Sevilla Diego Carlos ya doke Romelu Lukaku, abin da ya jawo bugun finareti, sannan wasan ya ƙare bayan Lukaku ya ci gida sakamakon watsiyar da Carlos ya yi.

Hakan na nufin Inter Milan za ta ci gaba da jiran lashe kofin Nahiyar Turai na tsawon aĆ™alla shekara 10 – tun bayan Champions League da ta lashe Ć™arĆ™ashin Jose Mourinho a 2010.

Finaretin da Lukaku ya ci ne ya fara buɗe wasan da ƙwallonsa ta 34 a dukkanin wasannin kakar bana kuma ta 11 a Europa na bana.

Luuk de Jong ne ya farke kuma ya ƙara dukaninsu da ka kafin Lukaku ya ci gidaa minti na 74.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...