Saudiya za ta taimakawa CBN da kuɗaɗen kasashen waje

Ƙasar Saudiya ta yi alkawarin samar da isassun kuɗaɗen kasar waje ga Najeriya domin taimakawa shirin Babban Bankin Najeriya(CBN) na kawo sauye kan yadda ake musayar kuɗaɗen waje.

Kasar ta Saudiyya dake da matukar arzikin man fetur ta kuma yi alkawarin zuba jari wajen farfaɗo da matatun man fetur na Najeriya.

Yarima mai jiran gado, Mohammed bin Salman shi ne ya yi wannan alkawarin a wata ganawa da suka yi da shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu a wurin taron kasashen Afrika da na Larabawa dake gudana a birnin Riyadh.

Jawabin hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a,Muhammad Idris Malagi ya fitar.

Yariman ya yabawa sauye-sauyen tattalin arziki da Tinubu yake aiwatarwa inda ya tabbatar da goyon bayan kasarsa wajen cimma nasarar sauye-sauyen.

More News

Mutum ɗaya ya mutu wasu sun jikkata a hatsarin motar tankar gas

Mutum ɗaya ya mutu a yayin da wasu biyu suka jikkata bayan da wata tankar gas tayi bindiga ta kama da wuta a Ita-Oshin...

Ɗan Boko Haram Ya Miƙa Kansa Ga Sojoji

Wani mamba a ƙungiyar ƴan ta'adda ta Boko Haram ma suna, Sajeh Yaga ya miƙa kansa ga dakarun rundunar Operation Haɗin Kai dake arewa...

EFCC ta kama wasu masu hada-hadar canjin kuɗaɗe

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta kama wasu mutane 34 da take zargi suna da hannu wajen yiwa...

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...