Saudi Arabia na maraba da masu aikin Umrah

Hajj

Saudiyya ta sanar da za ta kyale mazauna ƙasar su gudanar da ayyukan ibada na Umrah bayan ta dakatar da komai na tsawon watanni.

Hukumomin ƙasar sun ce daga baya za su kyale maniyyata dag ƙasashen waje su shiga ƙasar domin gudanar da ibadar wadda ta ke da muhimmanci ga Musulmin duniya, sai dai za ta ƙayyade yawan maniyyatan da yawan ƙasashen da za ta bari su shiga ƙasar.

Maniyatta da ke cikin Saudiyya na iya yin Umrah daga ranar 4 ga watan Oktoba, inda maniyattan da ke ƙasashen ƙetare kuwa sai sun jira zuwa ranar 1 ga watan Nuwamba kafin su sami izinin shiga ƙasar.

Ma’aikatar Aikin Hajji ta Saudiyya ta kuma bayyana cewa idan annobar korona ta gushe, za ta kyale dubban maniyatta daga ko’ina a duniya su ci gaba da ziyartar biranen Makkah da Madin domin gudanar da ibadunsu.

Musulmi na iya yin ibadar Umrah a duk lokacin da suka so, ba kamar aikin Hajji ba da ake iya yi sau É—aya kawai a kowace shekara.

Miliyoyin Musulmi daga sassan duniya kan tafi Saudiyya a kowace shekara domin sauke wannan muhimmiyar ibada da ke ta biyu ga aikin na Hajji a daraja.

Tun dai a watan Yulin bana hukumomin Saudiyya suka ɗauki matakai domin daƙile bazuwar annobar korona, A bana mutum 10,00 ne kawai suka yi aikin Hajji a maimakon kimanin miliyan biyu.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...