![](https://arewa.ng/storage/2020/09/Sarkin-Zazzau-Ya-Rasu-–-AREWA-News.jpg)
Inna lillahi wa Inna ilaihi raji’un Kullu nafsin za’iqatul maut
Allah Ya yi wa Mai Martaba Sarkin Zazzau Alh. Shehu Idris rasuwa a yau Lahadi a wani asibiti da ke Kaduna.
Sarkin ya rasu ne yana mai shekaru 84 da haihuwa.
Gwamna Kaduna, Malam Nasiru El-Rufai, shi ne ya sanar da rasuwar Sarkin a shafinsa na Facebook.