[ad_1]
Shugaban majalisar dattawa, Abubakar Bukola Saraki na duba yiwuwar yin takara da shugaban kasa Muhammad Buhari a zaben shekarar 2019.
Saraki wanda tun da fari ya nuna alamun neman zama shugaban kasa, ya fadawa jaridar Bloomberg cewa har yanzu yana cigaba da tattaunawa.
Duk acikin mako guda shugaban majalisar dattawan ya ziyarci tsohon shugaban kasa Ibrahim Badamasi Babangida da kuma Olusegun Obasanjo.
Saraki ya ce akwai buƙatar ya samu tikitin takarar shugaban kasa a jam’iyar PDP domin cika fatan da yake da shi na jagorancin kasarnan.
Makonni biyu da suka wuce ne shugaban majalisar dattawan ya sauya sheka daga jam’iyar APC ya zuwa PDP.
“Ina cigaba da tuntuba da kuma duba yiyuwar haka.Na yarda zan iya kawo sauyi,”aka jiyo shi yana fada.
“Jam’iyar PDP ta koyi darasi daga faduwar zabe da tayi a 2015 ina tunanin abin rashin dadi APC bata koyi wani darasi ba daga nasarar da tayi.”
[ad_2]