Sanata Imasuen ya koma jam’iyar APC daga LP

Neda Imasuen sanata mai wakiltar kudancin jihar Edo a majalisar dattawa a karkashin jam’iyar Labour Party ya sanar da ficewarsa daga jam’iyar inda ya koma APC.

Da yake magana a Benin babban birnin jihar, Imasuen ya ce rikicin cikin gida a jam’iyarsa ta LP shi ne ya sa ka shi daukar matakin fita daga jam’iyar.

Imasuen wanda shi ne shugaban kwamitin da’a da korafe-korafe a majalisar ya ce a ranar 12 ga watan Yuni ne zai sanar da sauya shekar ta sa a hukumance.

Sanatan ya ce sauya shekar ta sa na daga cikin wani bangare na bukukuwan da za a gudanar na murnar cikarsa shekaru biyu a majalisar dattawa.

Ya ce a matsayinsa na shugaban kwamitin dake karbar korafi a majalisar ya samu nasararar warware wasu matsaloli sama a 20 da aka kai korafinsu gaban majalisar.

Sauya shekar nasa na zuwa ne dai-dai lokacin da ake cigaba da samun yan jam’iyun adawa na komawa jam’iyar APC.

More from this stream

Recomended