Sadiya Faruq Ta Bayyana EFCC Kan Zargin Almundahanar Biliyan 37

Sadiya Umar tsohuwar ministan ma’aikatar jin kai ta amsa gayyatar da hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ta’annati ta yi mata.

Hukumar yaki da cin hancin na gudanar da bincike ne kan ma’aikatar da ta jagoranta a gwamnatin tsohon shugaban kasa, Muhammad Buhari kan zargin almundahanar naira biliyan 37.

Sadiya ta rike mukamin ministan daga shekarar 2019 zuwa 2023.

A ranar 4 ga watan Janairu ne hukumar ta EFCC ta nemi tsohuwar ministar da ta kai kanta ofishin hukumar ba tare da É“ata lokaci biyo bayan rahotannin dake cewa taki girmama gayyatar da EFCC tayi mata.

A martanin da ta mayar tsohuwar ministar ta ce rashin lafiya ce ta hana ta amsa gayyatar.

A yayin da ta bayyana a ofishin EFCC a ranar Litinin, Sadiya Faruq ta ce tana alfahari da cewa ta hidimtawa Najeriya a matsayin minista kuma a shirye take ta kare duk wasu ayyuka da tayi lokacin da take kan mulki.

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...