Rundunar Yan Sandan Jihar Kaduna Ta Gabatar da Wadanda Ake Zargi Da Kashe Jami’anta Hudu

[ad_1]

Rundunar ‘Yan-sandan jahar Kaduna ta ce ta kama wasu daga cikin tsagerun da ake zargi da hannu wajen kashe ‘yan-sanda hudu a kwanakin baya, sannan kuma ta kama wasu barayin mutane da motoci da sauran masu aikin assha a jahar.

Mukaddashin kwamishinan ‘yan-sandan jahar wanda kuma shine mataimakin kwamishina mai kula da kudi, DC Magaji Ahmed Kontagora ne ya yiwa manema labaru karin haske a Kaduna.

Ranar goma sha daya ga wannan wata na Augusta ne wasu yan-bindiga su ka tare ‘yan-sanda a yankin Jarkasa dake garin Rigasa, inda bayan sun yi misayar wuta na wani dogon lokaci aka kashe ‘yan-sanda guda hudu wanda tun daga nan rundunar ‘yan- sandan ke ta fafutukar ganin ta farke layar masu wannan barna.

Saurari rahoton Isa Lawal Ikara

[ad_2]

More News

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...

AMBALIYA: Bafarawa ya ba wa al’ummar Sokoto gudunmawar naira biliyan 1

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Attahiru Bafarawa, ya bayar da gudummawar Naira biliyan daya ga al’ummar Sokoto, domin rage radadin wannan annoba.An bayyana hakan...

Ƴanbindiga sun kai hari coci-coci a Kaduna, sun kuma yi garkuwa da mutane

Mutane 3 ne ake fargabar sun mutu, sannan an yi garkuwa da wasu 30 bayan wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a...