Rundunar Sojin Saman Najeriya Ta ce Ta Sami Gagarumar Nasara a Yakin Da Take Yi Da ‘Yan Ta’adda A Sokoto | VOA Hausa

A daidai lokacin da Rundunar sojin saman Najeriya ta ce ta sami gagarumar nasarori a yakin da take yi da ‘yan ta’adda a yankin gabashin jihar Sokoto, mazauna yankunan sun ce har yanzu ba za’a rasa fargaba ba, domin ‘yan bindigar suna nan kusa da jama’ar yankin.

Babban hafsan sojin saman Najeriya, Air marshall Sadiq Baba Abubakar shi ne ya furta batun samun nasarar a wurin bikin da rundunar sojin sama da ke jihar Sokoton ta gudanar don taya murnar Sallah ga sojojin da ke bakin daga a yankin.

Air marshall Sadiq Baba Abubakar, ta bakin kwamandan rundunar dabarun kai farmaki da jirage, AVM Olusegun Philip ya ce, aikin da mayakan saman suke gudanar wa ya taikamaka gaya wajen dakile ayukan ta’addanci a yankunan.

Wasu daga cikin mazauna yankunan sun shaidawa wakilin muryar Amurka cewa, sun gudanar da bikin sallah lafiya, ba tare da wani tashin hankali ba. Amma sun nuna damuwarsu da fargaba, domin a cewar su ‘yan bindigar suna kusa da yankunan nasu.

More News

Ƴan bindiga sun ƙone ginin hedkwatar ƙaramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu ƴanta’adda da ke da alaƙa da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa ƴan’adda a Borno, wani kwamanda ya miƙa wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...

Yadda wani adalin direba ya kawo cigiyar haka maƙare a kuɗi

Wani direban motar kasuwa ya mayarwa rundunar ‘yan sandan jihar Kano jakar da ta bata dauke da makudan kudade.  Direban mai suna Safiyanu Mohammed...