Rundunar sojin Najeriya ta musalta cewa Boko Haram sun kashe sojoji 30

[ad_1]








Aƙalla sojoji 30 aka rawaito an kashe a wani hari da yan kungiyar Boko Haram suka kai kan wani sansanin sojoji dake kauyen Zari a jihar Borno.

Rahotannin sun nuna cewa sojojin sunwa yankin dirar mikiya cikin manyan motoci inda suka ci karfin sansanin tare da korar mutanen kauyen baki dayansu.

Wata majiya ta shedawa jaridar Daily Trust cewa sojoji 20 aka jikkata a harin.

Sojojin sun janye daga sansanin tare da barin makamai masu yawa da yan ta’addar suka yi gaba da su.

An tura jirgin yaki ya zuwa yankin wanda ya taimaka wajen dakile harin.

“Mun rasa sojoji da dama a fadan da yawa daga cikinsu sun bace saboda har yanzu basu dawo sansanin soja dake Damasak ba ,”a cewar wata majiyar soja, haka kuma yan ta’addar sun yi awon gaba da makamai masu yawa.

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Juma’a amma ta gaza bayyana adadin yawan sojojin da tayi asara.

Mai magana da yawun rundunar Texas Chukwu ya ce yan ta’addar basu kai wa sojojin hari ba face sojojin ne suka kai musu farmaki.




[ad_2]

More News

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...

AMBALIYA: Bafarawa ya ba wa al’ummar Sokoto gudunmawar naira biliyan 1

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Attahiru Bafarawa, ya bayar da gudummawar Naira biliyan daya ga al’ummar Sokoto, domin rage radadin wannan annoba.An bayyana hakan...

Ƴanbindiga sun kai hari coci-coci a Kaduna, sun kuma yi garkuwa da mutane

Mutane 3 ne ake fargabar sun mutu, sannan an yi garkuwa da wasu 30 bayan wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a...