
Rundunar Sojan Saman Najeriya ta ce ta kaddamar da bincike kan rahoton dake cewa an samu asarar rayukan fararen hula a harin da jirgin yakin rundunar ya kai kan kasuwar Jilli dake kan iyakar jihohin Borno da Yobe.
Lamarin ya faru ne a ranar Asabar a kasuwar dake tsakanin ƙananan hukumomin Gubio a jihar Borno da kuma Geidam a jihar Yobe a lokacin farmaki kan mayakan Boko Haram.
A wata sanarwa da rundunar ta fitar a ranar Lahadi ta bakin,Shine Ejodame daraktan hulda da jama’a na rundunar ta ce ɗauki rahoton da matuƙar muhimmanci da tausayawa.
Ehimen ya ce babban hafsan rundunar ya bawa sashen dake binciken kai hari kan fararen hula umarnin gaggawa na zuwa wurin tare da gudanar da cikakken bincike.
Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International ta yi allawadai da harin da ta ce ya kashe fararen hula sama da 100.

