Rikicin Sudan:Rukuni Na Biyu Na Yan Najeriya Sun Sauka A Abuja

Rukuni na biyu na É—aliban Najeriya da ke gujewa rikicin Sudan sun sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja.

Hukumar NIDCOM dake kula da yan Najeriya mazauna ƙasashen waje ta ce yan Najeriya 130 da suka haɗa da mata 128 da kuma maza biyu sun taso daga filin jirgin saman garin Port Sudan a cikin jirgin kamfanin Tarco Airline inda suka sauka a filin jirgen saman Abuja da misalin karfe 03:15 na yamma.

Ana kuma saka ran jirgin kamfanin Azman da yanzu haka yake kasar Masar zai kwaso karin wasu yan Najeriyar zuwa gida.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...