Rikicin Sudan: Max Air Zai Kwaso Yan Najeriya 560 Daga Masar

Kamfanin jiragen sama na Max Air zai kwaso karin wasu yan Najeriya da rikicin Sudan ya rutsa da su.

Kamfanin ya bayyana haka ne cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis.

Sanarwar ta bayyana cewa kamfanin zai yi amfani da jirgin sa kirar Boeing 747-400 domin kaso yan Najeriya 560 da yanzu haka suke makale a Masar bayan tserewa rikicin na Sudan.

Kawo yanzu dai dubban yan Najeriya ne suke can kan iyakar Sudan da Masar inda suke jiran a kwaso su zuwa gida.

A jiya ne dai rukunin farko na yan Najeriya da aka kwaso suka sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja

More News

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...

NFF ta naÉ—a Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...