Real Madrid da Valladolid: Ko Real Madrid za ta hada maki uku kuwa? | BBC News

Real Madrid

Real Madrid za ta karbi bakuncin Real Valladolid a wasan mako na hudu a gasar La Liga da za su fafata ranar Laraba a Alfredo Di Stefano.

A kakar bara Real ta hada maki hudu a kan Valladolid, bayan da suka tashi kunnen doki 1-1 ranar 24 ga watan Agustan 2019 a karawar farko.

A wasa na biyu a La Liga da suka fafata a gidan Valladolid, Real ce ta yi nasara da ci 1-0 ranar 26 ga Janairun 2020.

Kuma Nacho Fernandez ne ya ci wa Real kwallon saura minti 12 a tashi daga wasan.

A kakar bana Madrid ta yi canjaras a gidan Real Sociedad ranar 26 ga watan Satumba, kwana shida tsakani ta je ta doke Real Betis da ci 3-2.

Tuni dai kocin Real Madrid, Zinedine Zidane ya bayyana ‘yan wasa 22 da za su fuskanci Valladolid.

Masu tsaron raga: Courtois, Lunin and Altube.

Masu tsaron baya: Carvajal, Sergio Ramos, R. Varane, Nacho, Marcelo, Odriozola and F. Mendy.

Masu buga tsakiya: Modrić, Casemiro, Valverde, Ødegaard and Isco.

Masu buga gaba: Benzema, Asensio, B. Mayoral, Lucas V., Jović, Vini Jr. and Rodrygo.

Wasu wasannin La Liga 10 da Real Madrid za ta buga nan gaba:

Lahadi 04 ga Oktoban 2020

Lahadi 18 ga Oktoban 2020

Lahadi 25 ga Oktobvan 2020

Lahadi 1 ga Nuwambar 2020

Lahadi 8 ga Nuwambar 2020

Lahadi 22 ga Nuwambar 2020

  • Villarreal da Real Madrid

Lahadi 29 ga Nuwambar 2020

Lahadi 6 ga Disambar 2020

Lahadi 13 ga Disambar 2020

  • Real Madrid da Atl Madrid

Lahadi 20 ga Disambar 2020

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...