Ranar Lahadi za mu yi Idi a Najeriya, inji Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar na III ya ce sai ranar Lahadi za a yi Sallar Idi a Najeriya sakamakon rashin ganin jaririn watan Shawwal a kasar.

A wata sanarwa da ta fito daga fadarsa, ta ce “fadar mai alfarma da kuma kwamitin ganin wata na kasa ba su samu labarin ganin watan Shawwal na shekarar 1441 ba daga ko’ina a fadin kasar, ranar Juma’a.

Saboda haka ranar Asabar za ta zama rana ta 30 ga watan Azumin Ramadan.”

Hakan ne ya sa Mai Alfarma Sarkin Musulmi da Majalisar Koli ta Addinin Musulunci suka yanke cewa ranar Lahadi 24 ga watan Mayu wadda ta yi daidai da 1 ga Shawwal 1441 ce ranar Idi a Najeriya.

Wannan dai na zuwa ne ‘yan sa’o’i bayan da kasar Saudiyya ta ce ba ta ga jaririn watan Shawwal ba a saboda haka za a yi Sallah ne ranar Lahadi.

Ita kuwa makwabciyar Najeriya, Jmahuriyar Nijar ta sanar da ganin watan na Shawwal inda za a yi Idi a ranar Asabar.

Ba wannan ne karon farko da ake samun babban ba tsakanin kasashen duniya dangane da ganin wata na fara Azumin Ramadan da kuma karkare shi.

Hakkin mallakar hoto
Sultanate

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...