Osimhen ya koma Galatasaray da wasa

Ɗan wasan gaba na Najeriya, Victor Osimhen ya isa ƙasar Turkiyya inda zai fara buga wasa a ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Galatasaray dake  ƙasar.

Da yake magana da manema labarai jim kaɗan bayan saukarsa a filin jirgin sama na Istanbul ya nuna murnarsa matuƙa kan irin tarbar da ya samu.

Dubban magoya bayan ƙungiyar ɗauke da ganguna  ne suka tarbe shi.

Ɗan wasan mai shekaru 25 ya koma ƙungiyar ne a matsayin aro daga ƙungiyar Napoli da yake buga wasansa acan bayan da dangantaka tayi tsami a tsakaninsu.

Ƙungiyar ta Æ™asar Turkiyya za ta dauki nauyin biyan albashin Osimhen a tsawon lokacin aron  amma kuma babu tilashin sai sun saye shi a Æ™arshen kakar wasannni.

More News

Atiku ya bayar da tallafin miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya bayar da gudunmawar naira miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri babban birnin...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

Mutanen Sokoto na ta murnar kashe ƙasurgumin ɗanbindigar nan Halilu Buzu

Mazauna yankin Sokoto da kewaye na murnar kashe wani kasurgumin shugaban ‘yan bindiga, Kachallah Halilu Buzu, da sojojin Najeriya suka yi a farmakin da...