Ododo: Bazan taba cin amanar Yahaya Bello BA tamkar uba yake a wurina

Usman Ododo, gwamnan jihar Kogi ya ce ba zai taba cin amanar Yahaya Bello ba wanda ya gaji kujerarsa a matsayin gwamnan jihar.

Ododo ya fadi haka ne a ranar Juma’a bayan wata ziyarar girmamawa da ya kai wa Abdullahi Umar Ganduje shugaban jam’iyar APC na kasa da kuma shugabannin jam’iyar na kasa a hedkwatar jam’iyar dake Abuja.

Gwamnan ya nuna matukar godiyarsa kan muhimmiyar  rawar da Bello ya taka wajen daukakarsa a siyasa inda ya kara da cewa biyayyarsa gare shi tana nan daram.

Ya kara da cewa Bello tamkar uba yake a wurinsa saboda shi ba a haife shi a cikin gidan masu kudi ba.

“Daga inda ya tsamo ni da kuma yadda Allah ya yi amfani da shi wajen daga darajata har yanzu yana cikin kwakwalwata  tamkar yanzu ya faru.Bazan taba manta asalina ba,” ya ce.

“Bazan taba yi ko iya cin amanarsa ba. Idan  kaga yaro yana fushi da mahaifinsa. To wannan yaron abinciki asalinsa,” ni ba irin wannan ba ne.

More from this stream

Recomended