NNPP ta dakatar da Kwankwaso saboda zargin cin dunduniyar jam’iyya

Kwamitin amintattu na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP, ta dakatar da dan takararta a zaben shugaban kasa da aka yi a ranar 25 ga watan Fabrairu, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, bisa zargin zagon ƙasa wa jam’iyyar.

Kwamitin ya kuma dakatar da kwamitin gudanarwa na kasa, wato National Working Committee, NWC.

Haka kuma ta nada sabon kwamitin shugabanni na kasa karkashin Dokta Agbo Major a matsayin shugaban riko na kasa da Mista Ogini Olaposi a matsayin mukaddashin sakataren kasa.

Rahotanni sun nuna cewa dakatarwar za ta yi aiki ne na tsawon watanni shida.

Da yake yi wa manema labarai jawabi a karshen taron da aka yi a Legas ranar Talata, sakataren kungiyar, Babayo Muhammed Abdulahi ya zargi Kwankwaso da tarayya da shugaban kasa Bola Tinubu, da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, da kuma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP) Mista Peter Obi, ba tare da izinin jam’iyya ba.

More News

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...

Ƴansanda sun kama likitan bogi

Rundunar ‘yan sanda ta Zone 2, Onikan, Legas, ta kama wani likitan jabu mai shekaru 37, kuma ma’aikacin lafiya, tare da zargin amfani da...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

Ƴan sanda sun kama masu garkuwa da mutane da suka yi bacci a lokacin da suke tsare da mutanen da suka sace

Jami'an Æ´an sanda sun samu nasarar kama wasu masu garkuwa da mutane bayan da suka buge da sharar bacci a lokacin da suke tsare...